Wednesday, 13 June 2018

An yanke hukuncin kisa Akan mutane buyer; Ko me dalili?

Kotu ta yanke hukuncin kisa Akan was mutane biyar a dalilin kashe wani makiyayi da sukayi.  Abin ya faru ne a kauyen Kadamun da ke karamar hukuman Demsa a jihar Adamawa. 

A zaman kotun ran sha biyu ga watan juni, alkali Mai Shari'a, Abdulaziz waziri yace Alex Amos, Holy Boniface, Alheri Phanuel, Jerry Gideon da Jari Sabagi da hanu dumu dumu akan Kisan wani makiyayi Mai suna Adamu Buba.

Hujjoji kwarara cewa sun Kai hari Kan makiyayan ne guda uku yanda suka sami nasaran kashe shi Buba din suka jefar da gawar a teku sannan suka hallaka shanu babu adadi. 

Allah ya kyauta. 

Send us your stories at 08068400069 or wazobiaanews@gmail.com

Ta mutu don neman a mata karin girman nono

Wata budurwa mai suna, June Wanza Mulupi, a kasar Nairobi Kenya ta Rasa rayuwanta a dalilin neman Karin girman nononta da take ganin girmansu sun kasa. Hakan ne yasa taje gun likitoci don a Kara Mata girman su Sabu da tsaro. 

KU KALLI YADDA TSOHON GWAMNA KE SHARBE KUKA A KOTU BAYAN DAURIN DA AKA ZARTAR A KANSA

SHI DAI SANATA JUSHUA DARIYE TSOHON GWAMNA NE A JIHAR PILATO A KARKASHIN JAM'IYYAR PDP. A HALIN YANZU, SHI SANATA NE MAI CI KUMA A KARKASHIN TUTAR JAM'IYYAR TA PDP DIN. JIM KADAN BAYAN GURFANAR DA SHI DA HUKUMAR EFCC TAYI, AN KAMASHI DA LAIFIN SAMA DA FADIN MAKUDAN KUDIN JIHAR A LOKACIN MULKIN SA. BAYAN KOTU TA ZARTAR DA HUKUNCIN DAURIN SHEKARU GOMA SHA HUDU AKAN SHI, BAI YI KASA A GWIWA BA SAI YA ZARCE DA KUKA HAR DA MAJINA. ALLAH YA KIYAYE MU DA CIN AMANAR KASA.

Sunday, 10 June 2018

KISAN KIYASHI A ZAMFARA. Daga Maibiredi Tashan Bagu

KISAN KIYASHI: AL'AMARIN 'YAN GUDUN HIJIRA NA MADA YA KARA MUNI
Labarin da ke shigo muna daga cikin garin Mada na nuna cewa Al'amari Ya kara baci A garin, Yanzun Haka, 'Yan Gudun Hijira sun Kai Dubu bakwai , 7000 ke jibge a makarantar primary school Ta Mada
Ko a daren Jiya Barayin Sun kashe Mutane Uku, Tare Da Jikkata Mutane Goma.

Saturday, 9 June 2018

KISAN KIYASHI: SAMA DA 'YAN GUDUN HIJIRA 300 KE ZAUNE A DAMBA, GWAMNATI BA SAN DA SU BA! Daga Maibiredi Tashan Bagu, gusau

KISAN KIYASHI: SAMA DA 'YAN GUDUN HIJIRA 300 KE ZAUNE A DAMBA, GWAMNATI BA SAN DA SU BA!
Yan gudun hijira Maza da mata Yara da mata tsoffi ke zaune da wani yanki na Damba a cikin garin Gusau.
'Yan gudun hijirar da da yawansu ya Kai 300 da suka fito Daga karamar Hukumar mulkin Bungudu, akalla sun shafe sama da Shekaru uku suna gudun hijira a cikin unguwar Damba.
A zantawarmu da su, lokacin da kungiyar Victims Of Violence Charity Foundation ta kawo masu tallafi, sun tabbatar muna da cewa, in ka Debe wannan kungiya da ta kawo masu dauki a shekarar da ta wuce, yau sama da shekaru uku su ke gudun hijira a wannan wuri, amma Gwamnati ko wata kungiya bata taba kawo masu dauki ba, Duk da fama da rashin Lafiya, abinci da rashin matsugunnin da su ke fama da shi.
'yan gudun hijirar sunyi Kira ga Gwamnatin jahar Zamfara da ta tarayya da sauran kungiyoyi. Da su

Wawanci ne danganta Ta'addanci ga musulunci: inji shugaban Kiristocin Duniya

Fafaroma Francis shugaban Kiristocin Duniya ya bayyana wa Duniya cewa masu danganta Ta'addanci ga musulunci ba komai bane saidai shashi fadi.
Bugu da kari, fafaroman wanda babban Jigo a mabiya darikar katolika yace addinai na duniya suna da mahimmin rawa da suke takawa wajen samar da zama lafya da koya al'adu kyawawa. 

Comments, share and Like. Send us your stories at +2348068400069

Friday, 8 June 2018

Jam'iyar apc Mai mulki tayi asarar wani jikon ta a jihar Kaduna.

Jam'iyar apc Mai mulki tayi asarar wani jikon ta a jihar Kaduna. She wannan jigon mai suna Ashiru Kudan yayi takaran neman kujeran Gwamnan jihar yadda Nasiru El_rufa'i, Gwamna Mai ci yanzu us kada shi.

A cewar sa, APC tajihar ta maida shi saniyar ware duk da wahalhalun da yasha yayin yakin neman zaben Gwamnan don son Jam'iyar amma kash, sun zuba masa kasa a ido.

An yanke hukuncin kisa Akan mutane buyer; Ko me dalili?

Kotu ta yanke hukuncin kisa Akan was mutane biyar a dalilin kashe wani makiyayi da sukayi.  Abin ya faru ne a kauyen Kadamun da ke karamar h...