Thursday, 24 August 2017

KUNGIYAR MATASAR AREWA TA JANYE WA’ADIN DA SUKA BAWA IYAMURAI. KO ME YASA?

KUNGIYAR MATASAR AREWA TA JANYE WA’ADIN DA SUKA BAWA IYAMURAI. KO ME YASA?
Kungiyar matasar arewa wacce akafi sani da “AREWA YOUTH CONSULTATIVE FORUM” a turance, tace ta dakatar da wa’adin da suka bawa iyamurai na barin yankin arewa kafin daya ga watan oktoban shekara 2017. Dama dai, kungiyar ta umarci kabilar Ibo (iyamurai) da subar yankin arewan sabida barazanar da shugaban mai fafutukar neman yankin Biafara, Namdi Kanu, yake yi wa ‘yan arewa mazauna yankin Ibon.  
Sanarwar janyewar dai ta biyo bayan tattaunawan da “yan kungiyan sukayi ne a zangon baki na Transcorp hotel da ke birnin Abuja.

A wata majiya daga dakin taron yace janyewar korar ba ta dindindin bane, bal, an dakatar ne na washin gadi kafin wasu lokuta a gani ko zasu ci gaba da bada wani wa’adin.    

No comments:

Post a Comment

An yanke hukuncin kisa Akan mutane buyer; Ko me dalili?

Kotu ta yanke hukuncin kisa Akan was mutane biyar a dalilin kashe wani makiyayi da sukayi.  Abin ya faru ne a kauyen Kadamun da ke karamar h...