IRAN TAYI GWAJIN AKAMI MAI LINZAMI
Duk da gaegadin da shugaban kasan Amurka, Mista Donald Trump
yake yi wa kasar Iran kan ci gaba da kirkiran makamin mai linzami, yau Iran
tayi gwanjin wani babban makami mai linzami. Wannan makamin da aka gwada
gudunsa yau an tabbabtar zaiyi cimma nisan kilomita dubu biyu daga wurin da aka
harba shi.
A ran sha tara ga wannan wata na satumba, Dunald Trump ya
zargi kasan Iran a matsayin kasa mai goyon bayan ta’addanci da ‘yan ta’adda. Kuma
ya kara da cewa mulkin da akeyi a Iran irin mulkin zalunci ne da babakere. Dunald
Trump yayi wannan jawabin ne a gaban shuwagabannin duniya a taron majalisan
dinkin duniya ta saba’in da dori.
A cewar sa, shugaban kasan Iran din, Rauhani, kasar sa bazata
daina keram makamin mai hadari ba don suna son habaka karfin sun a soji. Kuma Rauhani
ya mida martini wa Donald Trump a taron majalisar dinkin duniya cewa Dunald
Trump ba komai bane in banda jahili, marar wayo kuma mai nuna kiyayyarsa a
fili.
No comments:
Post a Comment