Wednesday, 26 July 2017

Boko Haram Sun Sace Masu Binciken Mai Guda Goma A  Jihar Borno


Boko Haram Sun Sace Masu Binciken Mai Guda Goma A  Jihar Borno

Kamfanin mai na tarayyar Najeriya, NNPC ya bayyana cewa wasu  mayakan Boko Haram sun yi awun gaba da  masu binciken mai fetur goma jihar Borno.
Rahotanni daga NNPC na cewa an yi awan gaba da mutanen ne bayan wani kwantan
bauna da aka yi musu a kusa da kauyen Jibi a yankin jihar ta Borno.

Har yanzu dai ba amo ba labarin wadanda aka sace din daga wandanda suka sace din ko kuma daga hukuma.
Wannan irin sace sace ya sha aukuwa a yankin Naija Delta mai arzikin mai. Haka yasa wasu na ganin ta iya yiyuwa ba yan Boko Haram din bane; masu neman suna da kudi ne kaman tsagerun yankin Neja Dalta.

Allah ya kyauta.

No comments:

Post a Comment

An yanke hukuncin kisa Akan mutane buyer; Ko me dalili?

Kotu ta yanke hukuncin kisa Akan was mutane biyar a dalilin kashe wani makiyayi da sukayi.  Abin ya faru ne a kauyen Kadamun da ke karamar h...